Skip to content
Opens in a new window
Mu zagaya Duniya: Fara yaƙin neman zaɓe da musayar yawu tsakanin Tinubu da Atiku
22 August 2026

Mu zagaya Duniya: Fara yaƙin neman zaɓe da musayar yawu tsakanin Tinubu da Atiku

Mu Zagaya Duniya

About

Shirin ''Mu Zagaya Duniya" tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako kamar yadda aka saba ya taɓo muhimman batutuwan da suka faru a makon da muke bankwana da shi a Najeriya da sauran ƙasashen Afrika da ma duniya baki ɗaya.

Cikin batutuwan da shirin ya taɓo akwai yakin neman zaben Najeriya, inda aka jiyo tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar na shan alwashin dawo da tallafin man fetur, da kuma raddin shugaba Tinubu kan wannan furuci, sai cikar shekaru goma sha biyar da kifar da gwamnatin shugaban Libya Muammar Ghaddafi, inda a yankin Gabas ta tsakiya muka tabo labarin Iran da ta sanya ladan makudan kudade ga duk wanda ya kamo mata sojojin Amurka dama sauran muhimman labarai daga sassa daban-daban na duniya.

Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.