Yadda satar jarabawa ke taka rawa wajen kassara ingancin ilimi a Najeriya
17 February 2026

Yadda satar jarabawa ke taka rawa wajen kassara ingancin ilimi a Najeriya

Ilimi Hasken Rayuwa

About

Shirin Ilimi hasken Rayuwa tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako ya mayar da hankali kan yadda satar jarabawa ke ƙoƙarin zama ruwan dare a makarantun sassan Najeriya, matsalar da ke ci gaba da illa ga ingancin ilimi a dukkan makarantu na ƙasar.

Akwai zarge-zargen da ke nuna cewa wasu daga cikin jami'an hukumomin da ke kula da shirya jarabawa a matakai daban-daban na taimakawa wannan mummunar ɗabi'a ta satar jarabawa ta hanyar fallasa amsoshin tambayoyin da ake shirin fitarwa ga ɗalibai.

Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.