Skip to content
Opens in a new window
Dr Kabiru Adamu kan ƙara yawan makaman da Najeriya ta sayo daga ƙetare
16 September 2026

Dr Kabiru Adamu kan ƙara yawan makaman da Najeriya ta sayo daga ƙetare

Bakonmu a Yau

About

Wani rahoton hukumar ƙididdiga ta Najeriya NBS ya nuna cewar, yawan makaman da gwamnatin ƙasar ke sayowa daga ƙetare da zummar inganta tsaro a ƙasar ya ƙaru da kaso 104, inda ta kashe Naira biliyan 55 a cikin watanni shidda na farkon wannan shekara, idan aka kwatanta da abinda aka kashe wajen sayen makaman a shekarar bara.

Tuni dai masana da sauran ƴan Najeriya suka fara bayyana ra’ayoyi mabanbanta kan rahoton, inda wasu ke yabawa, yayin da wasu ke ganin bai kamata a dogara da ƙasashen ƙetare wajen samar da makamai ba.

Kan haka Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Kabiru Adamu, shugaban kamfanin Beacon Consulting mai binciken tsaro a nahiyar Afrika.

Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu.............