
About
Bisa ga dukkan alamu za a iya samun fahintar juna tsakanin Nijar da kuma maƙociyarta Jamhuriyar Benin, waɗanda ke takun-saka tun bayan kifar da gwamanatin dimokuraɗiyyar ta Mohamed Bazoum yau kusan shekaru uku kenan.
Kasancewar Firaminsitan Nijar Mahamane Ali Lemine Zeine a wurin bikin rantsar da sabon shugaban Benin Romuald Wadagni, na ƙara nuni da cewa za a iya samun kusanci a tsakanin ɓangarorin biyu.
A game da haka ne Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Adamu Muhammadu Ɗan Madawa, ɗaya daga cikin shugabannin ƴan Nijar mazauna Najeriya.
Latsa alamar sauti don sauraren zantawarsu...