14 September 2026
Alhaji Ibrahim Muhammad kan yadda shirin samar da ɗan takarar adawa ɗaya a Najeriya ya rushe
Bakonmu a Yau
About
Hukumar Zaɓen Najeriya ta fitar da jerin sunayen mutane 18 da suka cancanci tsayawa takarar shugabancin ƙasar da mataimakansu, sai kuma wasu mutane dubu 4 da 860 da za su tsaya takarar neman kujerun Majalisun Tarayya a zaɓen da za a yi shekara mai zuwa.
Wannan dai na nuni da cewa yunƙurin ƴan adawa na fitar da ɗantakarar ɗaya tilo don tunkarar jam’iyyar mai mulki ya ci tura.
Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Ibrahim Muhammad, shugaban jam’iyyar AMP ɓangaren adawa reshen jihar Kebbi, domin jin matsayinsu dangane da haka.